Alhamis 18 Yuni 2026 - 17:43
Silsilar Tattaunawa Kan Mahdawiyya (40) | Imam – Bayyanar Rahamar Allah Marar Iyaka

Hauza/ Koda yake Imam Mahdi (A) yana cikin gaiba, amma shi kamar gajimaren rahama ne da ke ci gaba da zubar da albarka, yana ba wa hamadar rayuwar mutane rai da kuzari. Wanda ya yi asara shi ne wanda bai dandana wannan tushen ƙauna da jinƙai ba.

Kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Hauza ya ruwaito, ana gabatar da jerin bahasin Mahdawiyya mai taken “Zuwa ga Al’umma Mai Manufa”, da nufin yada koyarwa da ma’arifar da suka shafi Imam Mahdi (A.F), ga masu karatu masu daraja.

Daya daga cikin bangarorin da ba a cika sani ba game da Imam Mahdi (A) shi ne ƙauna da jinƙansa ga mutane. Abin takaici, tun da dadewa wasu suna bayyana shi ne kawai da takobi, zubar da jini, da ramuwar gayya, suna nuna shi da siffar tsauri. Alhali kuwa shi ne bayyanar rahamar Allah mara iyaka, uba mai tausayi ga al’umma, aboki mai kula da su, kuma jagora mai son alherinsu.

A cikin wani hadisul Ƙudusi, bayan ambaton Imamai ma’asumai (A), an ce:

«وَ أُکمِلُ ذَلِکَ بِابْنِهِ م‏حمد رَحْمَةً لِلْعَالَمِین‏.»

“Zan cika [jerin Imamai] da ɗansa Muhammad, a matsayin rahama ga dukkan halittu.” (Usul al-Kafi, Juzu'i na 1 shafi na 528)

Haka kuma a cikin wata magana daga Imam da kansa, ya ce:

«أَنَّ رَحْمَةَ رَبِّکُمْ وَسِعَتْ کُلَّ شَی‏ءٍ وَ أَنَا تِلْکَ الرَّحْمَة.» 

“Lallai rahamar Ubangijinku ta kewaye komai, kuma ni ne wannan rahamar.” (Bihar al-Anwar, juzu'i na 53, shafi na 11)

Haka kuma daga bayanan Ahlul Baiti (A) an ce:

«وَ أَشْفَقَ عَلَیهِمْ مِنْ آبَائِهِمْ وَ أُمَّهَاتِهِم‏.»

“Imam yana jinƙai ga mutane fiye da yadda iyayensu maza da mata suke yi.” (Bihar al-Anwar, juzu'i na 25, shafi na 117)

Imam Mahdi (A.F) babban mai bada tarbiyya ne, malami mai tausayi ga bil’adama, kuma uba mai ƙauna ga mutane. A kowane lokaci yana kula da abin da ya fi dacewa da su. Duk da cewa ba ya bukatar su, amma yana ba su mafi girman kulawa da jinƙai. Kamar yadda ya fada:

«لَوْ لَا مَا عِنْدَنَا مِنْ مَحَبَّةِ صَلَاحِکُمْ وَ رَحْمَتِکُمْ وَ الْإِشْفَاقِ عَلَیکُمْ لَکُنَّا عَنْ مُخَاطَبَتِکُمْ فِی شُغُل.»  

“Da ba domin muna son gyaran al’amuranku ba, kuma muna da rahama da tausayi gare ku, da mun shagaltu da abin da zai sa mu bar mu’amala da ku.” (Bihar al-Anwar, juzu'i na 53, shafi na 179)

Saboda haka, koda yake Imam Mahdi (A.F) yana cikin gaiba, amma shi kamar gajimaren rahama ne da ke ci gaba da zubo albarka, yana ba wa hamadar rayuwar mutane rai da sabon kuzari. Wanda ya kasance mai asara shi ne wanda bai dandani wannan tushen ƙauna da jinƙai ba, kuma bai more daɗin wannan soyayya ba.

«اللهم هَبْ لَنَا رَأْفَتَهُ وَ رَحْمَتَهُ وَ دُعَاءَهُ وَ خَیرَه‏.»

“Ya Allah! Ka ba mu damar samun tausayi, rahama, addu’a, da alherin Imam.” (Mafatih al‑Jinan, Addu’ar Nudba)

Wannan tattaunawa za ta ci gaba…

An ɗauko daga littafin “Negine Afarinesh” tare da ɗan gyara kaɗan

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha